Nura Isa S Garo
11(ZAHIRIN KAUNA LITTAFI NA DAYA, NA NURA S GARO) “wallahi Mama wata shari’a zamu shiga gobe kuma ban gama tattara bayanan da nake son samu ba shi ya sa na ce Barrister Halima ta biyomun yau da wuri mu fita kar lokaci ya kuremana” “Allah ya taimaka” Mahaifiyarta ta ce mata a takaice sannan ta mike daga zaunen da ta ke akan doguwar kujerar tana nuna mata dining inda abinci ke jere akai ta ci gaba da cewa, “sai muje ki ci abinci kyafi samun kuzarin gudanar da bincinken yadda ya kamata” “to Mama” Barrister Zahra ta amsa tana mai fadada murmushin kan fuskarta, ta mike daga tsugunnan da ta ke ta karasa kan dining table din ta samu kujerar kusa da Mahaifiyarta ta ja ta zauna sannan ta ja flask din shayi ta zuzzuba musu a kofuna kamar yadda suka saba. tsawon minti goma suka kwashe suna cin abincin bayan sun gama ne Zahra ta dauki wayarta tana kokarin kiran Halima ta jiyo sallamarta don haka ta mayar da wayar cikin jaka sannan ta saita kallonta zuwa bakin kofar shigowa gidan inda suka hada ido da Halima a kokarin da ta ke na shigowa da murmushin a kan fuskarta ta tsugunna har kasa ta gaishe da Mahaifiyar Zahra sannan ta tashi ta mikawa Zahra hannu sukai musabiha sunawa junansu murmushi, Zahra ta nuna mata kujera ta ce, “bismilla ki fara cin abinci sai mu tafi ko?” Barrister Halima ta girgiza kai tana murmushi ta ce, “kema kinsan bayadda za a yi Hajiya ta barni na fito daga gida batare da na karya ba, wallahi na koshi sosai cikinnan nawa ba masaka tsinke” “ya yi kyau!” Barrister Zahra ta ce lokacin da ta ke kokarin mikewa daga kan kujerar da ta ke zaune ta kalli Mahaifiyarta wacce ta zuba musu ido tana kallonsu cikin fara’a da sakin fuska. Ta ce, “to Mama zamu tafi” Justice Aisha ta kalleta tana murmushi ta ce, “Allah ya dawo da ku lafiya ya bada sa’a. haka nake son mutum da bada himma akan aikinsa. Har kun tunomun nima lokacin da nake ganiyar aikina na shari’a inhar ina da case a kotu hankalina baya kwanciya sai na ga na gama” Gaba daya sukai dariya ba tare da sunyi maganaba hakance ta sa Justice Aisha kara kallonsu a karo na biyu ta ce, 12(ZAHIRIN KAUNA LITTAFI NA DAYA, NA NURA S GARO) “sai kun dawo ‘ya’yannan amman don Allah ku yi kokari ku fitar da mazajen aure dan ba mayar da hankali akan aikin kawai nake son naga kunyiba ina son na ga kowacce ta kawomun mijin da za ta aura” Dariya suka karayi lokacin da suka juya suka fara tafiya da zummar fita daga cikin falon har sunkai bakin kofa Zahra ta waigo ta kalli Mahaifiyarta da guntun murmushinta ta ce, “ki kwantar da hankalinki Mamana ana gama wannan shari’ar insha Allah duk zamu gabato miki da surukanki ki tantancesu in sun cancanta ki basu in basu cancantaba mu kawo miki wasu” “Allah ya sa” Justice Aisha ta amsa cikin jin dadin amsar da ‘yarta ta bata domin a koda yaushe burinta bai wuce ta ga ‘yammatan biyu sun tsayar da mazajen aureba ganin tsayin lokacin da suka kwashe amman ba wacce ta ke zancen aure. Zahra da Halima sukai murmushi sannan suka fita daga cikin gidan suka karasa tsakiyar farfajiyar da motocin ke ajje suka shiga Motar Zahra ta jasu mai gadi ya bude musu gate suka fita. A hankula cikin nutsuwa Zahra ta ke jan motar lokacin da ta ke sauka daga cikin layinsu da ke kan titin President Avenue, Nassarawa G.R.A Kano ta juya sitiyarin motar suka hau tiin Hadejia Road. sun fara tafiya ne Halima ta kalli Zahra tana sassauta murmushin kan fuskata ta ce, “yanzu ta ina zamu fara?” Zahra ta waiga ta kalleta sannan ta mayar da hankalinta kan tukin da ta ke ta ce, “nan bampai zamu shiga kin san a nan suka ajjeshi sai gobe in an kaishi kotu dagacan za a zarce da shi sashin masu manyan laifika na bursin din kurmawa” “to Allah ya kiyaye” Halima ta ce, “ameen” Zahra ta amsa mata cikin nutsuwa tare da mayar da hankalinta kan tukin da ta ke lokacin da ta ke karya kwana domin hawa kan titin mission road. Tafiyar minti biyar ce ta kaisu sashen masu manyan laifuka na ofishin ‘yan sandan kasancewar babu nisa a tsakaninsu, Zahra ta samu waje ta yi parking a wajen da aka tanada domin ajje motoci sannan suka fito suna tafiya cikin nutsuwa suka jera domin shiga cikin ofishin ‘yan sandan. 13(ZAHIRIN KAUNA LITTAFI NA DAYA, NA NURA S GARO) Kai tsaye sashen masu kula da manyan laifi suka tunkara kasancewar ba wannan ba ne karon farko da suka fara shiga cikin ofishin kusanma ya zamar musu jiki domin duk wani babban laifi tanan suke fara bincikensa kafun su shiga kotu. Inspector Bashir suka tarar yana zaune a kan kujerarsa ya dunkufar da kai yana rubuce-rubuce, sallarmar da su Zahra suka yi ce ta sa ya dago da kansa da sauri da murmushi a kanfuskarsa ya amsa musu domin sun saba da shi sosai. “lallai yau muna da manyan baki, Barrister Zahra, Barrister Halima sannunku da zuwa” “yauwa sannunka da aiki Bashir” Barrister Zahra ta amsa mishi da murmushi a kan fuskarta lokacin da suke kokarin zama a kan kujerun da ke jere a gaban table din ofishinnasa. Da sauri Inspector Bashir ya mike yana cewa, “bari na kawo muku lemo” “a’a Inspector barshi kawai yanzu muka gama karyawa sannan muka fito mungode” Barrister Halima ce ta dakatar da shi don haka ya koma ya zauna tare da nutsuwa ya basu dukkan hankalinsa. Barrister Zahra ce ta yi gyaran murya lokacin da taga Inspector bashir ya nutsu yana sauraronsu sannan ta fara da cewa, “Bashir daman muna da wani case ne wanda za a shiga kotu gobe, shi ne muka biyo bayan wanda ake zargi domin yi mishi wasu tambayoyi” Inspector Bashir ya daga mata kai cikin girmamawa tare da janyo Computer da ke gabansa yana kallo ya ce, “haka ne Hajiya, ya sunan suspect din na duba muku?” “Alhaji Mukhtar Mai Gaskiya” da sauri Inspector Bashir ya kalli Barrister Zahra da alamun damuwa akan fuskarsa ya ce, “Hajiya anya kuwa kin san Barristan da zaki kara da shi a kotu kuwa?” Barrister Zahra ta kalli Inspector Bashir babu alamun faduwar gaba a kan fuskarta ta ce, “eh Barrister Haidar ko?” “eh shi ne” Inspector Bashir ya bata amsa har a lokacin da alamun damuwar a kan fuskarsa. Barrister Zahra da Halima sukai murmushi cikin nuna karfin gwiwa suka kalli juna sannan suka mayar da kallonsu kan Inspector Bashir, Barrister Zahra ta ce, 14(ZAHIRIN KAUNA LITTAFI NA DAYA, NA NURA S GARO) “na sani, ai shari’a ce Inspector ba da wanda bata hadawa. takan hada Uba da [ansa ko Miji da Matarsa don haka ba laifi ba ne dan Malami da [alibarsa sun goga a wannan karon” Inspector Bashir ya gyada mata kai ya ce, “haka ne Hajiya, nima ba wani abu na gujemiki ba sai record nasan dukkan wani lauya yana takama da irin nasarorin da ya yi a shari’arsa sannan yana kiyayewa domin kare darajarsa” Barrister Zahra ta ce, “haka maganarka ta ke, kamar yadda yanzunma Allah ne kadai ya san mai gaskiya da kuma wanda zai yi nasara” “to Allah ya bada sa’a” Bashir ya ce, sannan ya mayar da hankalinsa wajen shigar da sunan da ya ke a cikin computar bayan ya gama ne ya mike tsaye jikinsa ba kwari ya ce, “muje na kaiku inda ya ke” “to Bashir mungode” Suka ce mishi a tare lokacin da suke mikewa tsaye, Bashir ya shiga gaba suna biye da shi a baya har dakin da aka kulle Alhaji Mukhtar, wanda suka tarar da shi yana zaune ya dunkufar da kai tare da juyawa kofar dakin baya, ya yi shiru baya ko kwakwkwaran motsi. Inspector Bashir ya kallesu ya ce, “to Hajiya ni zan koma sai kun fito” “mun gode” Suka amsa mishi a tare Bashir ya juya ya tafi ya barsu a tsaye a bakin kofar dakin da Alhaji Mukhtar ke kulle inda suka zubawa dattijon mutumin ido suna kallonshi na dan wani lokaci ba tare da sun yi mishi maganaba. Sun kwashe tsawon minti biyu zuwa uku bawanda ya yi magana sannan Barrister Zahra ta yi gyaran murya tare da yi mishi sallama. “assalamu alaika” “ameen wa’alaikumussalam” Tattausar muryar dattijon ta daki dodan kunnensu, wanda ke magana cikin nutsuwa da kamala tamkar ba shi ake zargi da hukuncin kisan kai ba. Barrister Zahra ce ta ci gaba da magana da cewa, “sunana Barrister Zahra Muhammad, wannan kuma abokiyar aikina ce Barrister Halima Mahmoud. Mu ne lauyoyin da zamu kareka a shari’ar da za a gudanar gobe in Allah ya kaimu shi ne muka zo domin mu yi maka wasu tambayoyi da muke fatan zaka bamu hadin kai domin mu gudanar da aikinmu cikin nasara” 15(ZAHIRIN KAUNA LITTAFI NA DAYA, NA NURA S GARO) Barrister Zahra ta kai karshen maganar da ta ke amman tamkar tana fadawa dutse domin dattijon mutumin ko kwakwkwaran motsi bai yi ba tun daga amsa sallamar da ya yi ballantana ya waigo ya kulasu kamar yadda suka bukataba. “danka Umar Mukhtar shi ya daukemu a matsayin lauyoyin da zamu kareka” Ambaton sunan ‘danka Umar Mukhtar’ da Barrister Zahra ta yi ne ya sa a hankali dattijon mutumin ya waigo cikin nutsuwa ya kallesu da tattausan murmushi a kan fuskarsa, suka bishi da kallo a tare. Fari ne, yana da doguwar fuska mai cike da farar kasumba. Kallo daya zaka yi mishi ka fahimci akwai nutsuwa da jin dadi a tattare da shi, ga wani tattausan murmushi bayyane a kan fuskarsa wanda suka kasa gane murmushin me ya ke. ya dauki wasu ‘yan dakiku yana kare musu kallo yayinda murmushin kan fuskarsa ke kara fadada sannan ya taso tsam daga inda ya ke zaune, ya karasa bakin kofar ya dafa karfen da ya yi mishi iyaka da su Barrister Zahra. “barkanku da zuwa” Alhaji Mukhtar ya katse musu tunanin da suke ta hanyar yi musu magana sannan ya zuba musu ido yana kallonsu. “barka dai Baba” Barrister Halima ta yi karfin halin amsa mishi sannan ta sa hannu ta ta6a Barrister Zahra ganin ta kurawa dattijon mutumin ido tana kallonshi cikin mamaki bata ko kiftawa. Ganin Barrister Zahra ta dan nutsu ne ya sa Halima ta mayar da kallonta kan dattijon mutumin cikin tausasa murya domin ba shi girmansa ta fara yi mishi magana da cewa, “Baba wasu tambayoyi muke son yi maka, muna fatan zaka bamu hadin kai ka fadamana gaskiyar abunda ka sani” Alhaji Mukhtar ya fadada murmushin kan fuskarsa ya ce, “insha Allahu ‘yata, zan baku cikakken bayani duk da nasan [ana bai turoku wajena domin ku yi nasara ba, ya turomun ku ne kawai domin ya nunamun soyayya da kulawa” Mamakin Barrister Zahra ya kara munana jin bayanin da ke fita daga cikin bakin Alhaji Mukhtar, lokaci daya duk ta dabarbarce ta kasa yimai tambayar da ta ke son yi mishi. Barrister Halima ce ta kara yin ta maza a karo na biyu ta ce,11(ZAHIRIN KAUNA LITTAFI NA DAYA, NA NURA S GARO) “wallahi Mama wata shari’a zamu shiga gobe kuma ban gama tattara bayanan da nake son samu ba shi ya sa na ce Barrister Halima ta biyomun yau da wuri mu fita kar lokaci ya kuremana” “Allah ya taimaka” Mahaifiyarta ta ce mata a takaice sannan ta mike daga zaunen da ta ke akan doguwar kujerar tana nuna mata dining inda abinci ke jere akai ta ci gaba da cewa, “sai muje ki ci abinci kyafi samun kuzarin gudanar da bincinken yadda ya kamata” “to Mama” Barrister Zahra ta amsa tana mai fadada murmushin kan fuskarta, ta mike daga tsugunnan da ta ke ta karasa kan dining table din ta samu kujerar kusa da Mahaifiyarta ta ja ta zauna sannan ta ja flask din shayi ta zuzzuba musu a kofuna kamar yadda suka saba. tsawon minti goma suka kwashe suna cin abincin bayan sun gama ne Zahra ta dauki wayarta tana kokarin kiran Halima ta jiyo sallamarta don haka ta mayar da wayar cikin jaka sannan ta saita kallonta zuwa bakin kofar shigowa gidan inda suka hada ido da Halima a kokarin da ta ke na shigowa da murmushin a kan fuskarta ta tsugunna har kasa ta gaishe da Mahaifiyar Zahra sannan ta tashi ta mikawa Zahra hannu sukai musabiha sunawa junansu murmushi, Zahra ta nuna mata kujera ta ce, “bismilla ki fara cin abinci sai mu tafi ko?” Barrister Halima ta girgiza kai tana murmushi ta ce, “kema kinsan bayadda za a yi Hajiya ta barni na fito daga gida batare da na karya ba, wallahi na koshi sosai cikinnan nawa ba masaka tsinke” “ya yi kyau!” Barrister Zahra ta ce lokacin da ta ke kokarin mikewa daga kan kujerar da ta ke zaune ta kalli Mahaifiyarta wacce ta zuba musu ido tana kallonsu cikin fara’a da sakin fuska. Ta ce, “to Mama zamu tafi” Justice Aisha ta kalleta tana murmushi ta ce, “Allah ya dawo da ku lafiya ya bada sa’a. haka nake son mutum da bada himma akan aikinsa. Har kun tunomun nima lokacin da nake ganiyar aikina na shari’a inhar ina da case a kotu hankalina baya kwanciya sai na ga na gama” Gaba daya sukai dariya ba tare da sunyi maganaba hakance ta sa Justice Aisha kara kallonsu a karo na biyu ta ce, 12(ZAHIRIN KAUNA LITTAFI NA DAYA, NA NURA S GARO) “sai kun dawo ‘ya’yannan amman don Allah ku yi kokari ku fitar da mazajen aure dan ba mayar da hankali akan aikin kawai nake son naga kunyiba ina son na ga kowacce ta kawomun mijin da za ta aura” Dariya suka karayi lokacin da suka juya suka fara tafiya da zummar fita daga cikin falon har sunkai bakin kofa Zahra ta waigo ta kalli Mahaifiyarta da guntun murmushinta ta ce, “ki kwantar da hankalinki Mamana ana gama wannan shari’ar insha Allah duk zamu gabato miki da surukanki ki tantancesu in sun cancanta ki basu in basu cancantaba mu kawo miki wasu” “Allah ya sa” Justice Aisha ta amsa cikin jin dadin amsar da ‘yarta ta bata domin a koda yaushe burinta bai wuce ta ga ‘yammatan biyu sun tsayar da mazajen aureba ganin tsayin lokacin da suka kwashe amman ba wacce ta ke zancen aure. Zahra da Halima sukai murmushi sannan suka fita daga cikin gidan suka karasa tsakiyar farfajiyar da motocin ke ajje suka shiga Motar Zahra ta jasu mai gadi ya bude musu gate suka fita. A hankula cikin nutsuwa Zahra ta ke jan motar lokacin da ta ke sauka daga cikin layinsu da ke kan titin President Avenue, Nassarawa G.R.A Kano ta juya sitiyarin motar suka hau tiin Hadejia Road. sun fara tafiya ne Halima ta kalli Zahra tana sassauta murmushin kan fuskata ta ce, “yanzu ta ina zamu fara?” Zahra ta waiga ta kalleta sannan ta mayar da hankalinta kan tukin da ta ke ta ce, “nan bampai zamu shiga kin san a nan suka ajjeshi sai gobe in an kaishi kotu dagacan za a zarce da shi sashin masu manyan laifika na bursin din kurmawa” “to Allah ya kiyaye” Halima ta ce, “ameen” Zahra ta amsa mata cikin nutsuwa tare da mayar da hankalinta kan tukin da ta ke lokacin da ta ke karya kwana domin hawa kan titin mission road. Tafiyar minti biyar ce ta kaisu sashen masu manyan laifuka na ofishin ‘yan sandan kasancewar babu nisa a tsakaninsu, Zahra ta samu waje ta yi parking a wajen da aka tanada domin ajje motoci sannan suka fito suna tafiya cikin nutsuwa suka jera domin shiga cikin ofishin ‘yan sandan. 13(ZAHIRIN KAUNA LITTAFI NA DAYA, NA NURA S GARO) Kai tsaye sashen masu kula da manyan laifi suka tunkara kasancewar ba wannan ba ne karon farko da suka fara shiga cikin ofishin kusanma ya zamar musu jiki domin duk wani babban laifi tanan suke fara bincikensa kafun su shiga kotu. Inspector Bashir suka tarar yana zaune a kan kujerarsa ya dunkufar da kai yana rubuce-rubuce, sallarmar da su Zahra suka yi ce ta sa ya dago da kansa da sauri da murmushi a kanfuskarsa ya amsa musu domin sun saba da shi sosai. “lallai yau muna da manyan baki, Barrister Zahra, Barrister Halima sannunku da zuwa” “yauwa sannunka da aiki Bashir” Barrister Zahra ta amsa mishi da murmushi a kan fuskarta lokacin da suke kokarin zama a kan kujerun da ke jere a gaban table din ofishinnasa. Da sauri Inspector Bashir ya mike yana cewa, “bari na kawo muku lemo” “a’a Inspector barshi kawai yanzu muka gama karyawa sannan muka fito mungode” Barrister Halima ce ta dakatar da shi don haka ya koma ya zauna tare da nutsuwa ya basu dukkan hankalinsa. Barrister Zahra ce ta yi gyaran murya lokacin da taga Inspector bashir ya nutsu yana sauraronsu sannan ta fara da cewa, “Bashir daman muna da wani case ne wanda za a shiga kotu gobe, shi ne muka biyo bayan wanda ake zargi domin yi mishi wasu tambayoyi” Inspector Bashir ya daga mata kai cikin girmamawa tare da janyo Computer da ke gabansa yana kallo ya ce, “haka ne Hajiya, ya sunan suspect din na duba muku?” “Alhaji Mukhtar Mai Gaskiya” da sauri Inspector Bashir ya kalli Barrister Zahra da alamun damuwa akan fuskarsa ya ce, “Hajiya anya kuwa kin san Barristan da zaki kara da shi a kotu kuwa?” Barrister Zahra ta kalli Inspector Bashir babu alamun faduwar gaba a kan fuskarta ta ce, “eh Barrister Haidar ko?” “eh shi ne” Inspector Bashir ya bata amsa har a lokacin da alamun damuwar a kan fuskarsa. Barrister Zahra da Halima sukai murmushi cikin nuna karfin gwiwa suka kalli juna sannan suka mayar da kallonsu kan Inspector Bashir, Barrister Zahra ta ce, 14(ZAHIRIN KAUNA LITTAFI NA DAYA, NA NURA S GARO) “na sani, ai shari’a ce Inspector ba da wanda bata hadawa. takan hada Uba da [ansa ko Miji da Matarsa don haka ba laifi ba ne dan Malami da [alibarsa sun goga a wannan karon” Inspector Bashir ya gyada mata kai ya ce, “haka ne Hajiya, nima ba wani abu na gujemiki ba sai record nasan dukkan wani lauya yana takama da irin nasarorin da ya yi a shari’arsa sannan yana kiyayewa domin kare darajarsa” Barrister Zahra ta ce, “haka maganarka ta ke, kamar yadda yanzunma Allah ne kadai ya san mai gaskiya da kuma wanda zai yi nasara” “to Allah ya bada sa’a” Bashir ya ce, sannan ya mayar da hankalinsa wajen shigar da sunan da ya ke a cikin computar bayan ya gama ne ya mike tsaye jikinsa ba kwari ya ce, “muje na kaiku inda ya ke” “to Bashir mungode” Suka ce mishi a tare lokacin da suke mikewa tsaye, Bashir ya shiga gaba suna biye da shi a baya har dakin da aka kulle Alhaji Mukhtar, wanda suka tarar da shi yana zaune ya dunkufar da kai tare da juyawa kofar dakin baya, ya yi shiru baya ko kwakwkwaran motsi. Inspector Bashir ya kallesu ya ce, “to Hajiya ni zan koma sai kun fito” “mun gode” Suka amsa mishi a tare Bashir ya juya ya tafi ya barsu a tsaye a bakin kofar dakin da Alhaji Mukhtar ke kulle inda suka zubawa dattijon mutumin ido suna kallonshi na dan wani lokaci ba tare da sun yi mishi maganaba. Sun kwashe tsawon minti biyu zuwa uku bawanda ya yi magana sannan Barrister Zahra ta yi gyaran murya tare da yi mishi sallama. “assalamu alaika” “ameen wa’alaikumussalam” Tattausar muryar dattijon ta daki dodan kunnensu, wanda ke magana cikin nutsuwa da kamala tamkar ba shi ake zargi da hukuncin kisan kai ba. Barrister Zahra ce ta ci gaba da magana da cewa, “sunana Barrister Zahra Muhammad, wannan kuma abokiyar aikina ce Barrister Halima Mahmoud. Mu ne lauyoyin da zamu kareka a shari’ar da za a gudanar gobe in Allah ya kaimu shi ne muka zo domin mu yi maka wasu tambayoyi da muke fatan zaka bamu hadin kai domin mu gudanar da aikinmu cikin nasara” 15(ZAHIRIN KAUNA LITTAFI NA DAYA, NA NURA S GARO) Barrister Zahra ta kai karshen maganar da ta ke amman tamkar tana fadawa dutse domin dattijon mutumin ko kwakwkwaran motsi bai yi ba tun daga amsa sallamar da ya yi ballantana ya waigo ya kulasu kamar yadda suka bukataba. “danka Umar Mukhtar shi ya daukemu a matsayin lauyoyin da zamu kareka” Ambaton sunan ‘danka Umar Mukhtar’ da Barrister Zahra ta yi ne ya sa a hankali dattijon mutumin ya waigo cikin nutsuwa ya kallesu da tattausan murmushi a kan fuskarsa, suka bishi da kallo a tare. Fari ne, yana da doguwar fuska mai cike da farar kasumba. Kallo daya zaka yi mishi ka fahimci akwai nutsuwa da jin dadi a tattare da shi, ga wani tattausan murmushi bayyane a kan fuskarsa wanda suka kasa gane murmushin me ya ke. ya dauki wasu ‘yan dakiku yana kare musu kallo yayinda murmushin kan fuskarsa ke kara fadada sannan ya taso tsam daga inda ya ke zaune, ya karasa bakin kofar ya dafa karfen da ya yi mishi iyaka da su Barrister Zahra. “barkanku da zuwa” Alhaji Mukhtar ya katse musu tunanin da suke ta hanyar yi musu magana sannan ya zuba musu ido yana kallonsu. “barka dai Baba” Barrister Halima ta yi karfin halin amsa mishi sannan ta sa hannu ta ta6a Barrister Zahra ganin ta kurawa dattijon mutumin ido tana kallonshi cikin mamaki bata ko kiftawa. Ganin Barrister Zahra ta dan nutsu ne ya sa Halima ta mayar da kallonta kan dattijon mutumin cikin tausasa murya domin ba shi girmansa ta fara yi mishi magana da cewa, “Baba wasu tambayoyi muke son yi maka, muna fatan zaka bamu hadin kai ka fadamana gaskiyar abunda ka sani” Alhaji Mukhtar ya fadada murmushin kan fuskarsa ya ce, “insha Allahu ‘yata, zan baku cikakken bayani duk da nasan [ana bai turoku wajena domin ku yi nasara ba, ya turomun ku ne kawai domin ya nunamun soyayya da kulawa” Mamakin Barrister Zahra ya kara munana jin bayanin da ke fita daga cikin bakin Alhaji Mukhtar, lokaci daya duk ta dabarbarce ta kasa yimai tambayar da ta ke son yi mishi. Barrister Halima ce ta kara yin ta maza a karo na biyu ta ce,11(ZAHIRIN KAUNA LITTAFI NA DAYA, NA NURA S GARO) “wallahi Mama wata shari’a zamu shiga gobe kuma ban gama tattara bayanan da nake son samu ba shi ya sa na ce Barrister Halima ta biyomun yau da wuri mu fita kar lokaci ya kuremana” “Allah ya taimaka” Mahaifiyarta ta ce mata a takaice sannan ta mike daga zaunen da ta ke akan doguwar kujerar tana nuna mata dining inda abinci ke jere akai ta ci gaba da cewa, “sai muje ki ci abinci kyafi samun kuzarin gudanar da bincinken yadda ya kamata” “to Mama” Barrister Zahra ta amsa tana mai fadada murmushin kan fuskarta, ta mike daga tsugunnan da ta ke ta karasa kan dining table din ta samu kujerar kusa da Mahaifiyarta ta ja ta zauna sannan ta ja flask din shayi ta zuzzuba musu a kofuna kamar yadda suka saba. tsawon minti goma suka kwashe suna cin abincin bayan sun gama ne Zahra ta dauki wayarta tana kokarin kiran Halima ta jiyo sallamarta don haka ta mayar da wayar cikin jaka sannan ta saita kallonta zuwa bakin kofar shigowa gidan inda suka hada ido da Halima a kokarin da ta ke na shigowa da murmushin a kan fuskarta ta tsugunna har kasa ta gaishe da Mahaifiyar Zahra sannan ta tashi ta mikawa Zahra hannu sukai musabiha sunawa junansu murmushi, Zahra ta nuna mata kujera ta ce, “bismilla ki fara cin abinci sai mu tafi ko?” Barrister Halima ta girgiza kai tana murmushi ta ce, “kema kinsan bayadda za a yi Hajiya ta barni na fito daga gida batare da na karya ba, wallahi na koshi sosai cikinnan nawa ba masaka tsinke” “ya yi kyau!” Barrister Zahra ta ce lokacin da ta ke kokarin mikewa daga kan kujerar da ta ke zaune ta kalli Mahaifiyarta wacce ta zuba musu ido tana kallonsu cikin fara’a da sakin fuska. Ta ce, “to Mama zamu tafi” Justice Aisha ta kalleta tana murmushi ta ce, “Allah ya dawo da ku lafiya ya bada sa’a. haka nake son mutum da bada himma akan aikinsa. Har kun tunomun nima lokacin da nake ganiyar aikina na shari’a inhar ina da case a kotu hankalina baya kwanciya sai na ga na gama” Gaba daya sukai dariya ba tare da sunyi maganaba hakance ta sa Justice Aisha kara kallonsu a karo na biyu ta ce, 12(ZAHIRIN KAUNA LITTAFI NA DAYA, NA NURA S GARO) “sai kun dawo ‘ya’yannan amman don Allah ku yi kokari ku fitar da mazajen aure dan ba mayar da hankali akan aikin kawai nake son naga kunyiba ina son na ga kowacce ta kawomun mijin da za ta aura” Dariya suka karayi lokacin da suka juya suka fara tafiya da zummar fita daga cikin falon har sunkai bakin kofa Zahra ta waigo ta kalli Mahaifiyarta da guntun murmushinta ta ce, “ki kwantar da hankalinki Mamana ana gama wannan shari’ar insha Allah duk zamu gabato miki da surukanki ki tantancesu in sun cancanta ki basu in basu cancantaba mu kawo miki wasu” “Allah ya sa” Justice Aisha ta amsa cikin jin dadin amsar da ‘yarta ta bata domin a koda yaushe burinta bai wuce ta ga ‘yammatan biyu sun tsayar da mazajen aureba ganin tsayin lokacin da suka kwashe amman ba wacce ta ke zancen aure. Zahra da Halima sukai murmushi sannan suka fita daga cikin gidan suka karasa tsakiyar farfajiyar da motocin ke ajje suka shiga Motar Zahra ta jasu mai gadi ya bude musu gate suka fita. A hankula cikin nutsuwa Zahra ta ke jan motar lokacin da ta ke sauka daga cikin layinsu da ke kan titin President Avenue, Nassarawa G.R.A Kano ta juya sitiyarin motar suka hau tiin Hadejia Road. sun fara tafiya ne Halima ta kalli Zahra tana sassauta murmushin kan fuskata ta ce, “yanzu ta ina zamu fara?” Zahra ta waiga ta kalleta sannan ta mayar da hankalinta kan tukin da ta ke ta ce, “nan bampai zamu shiga kin san a nan suka ajjeshi sai gobe in an kaishi kotu dagacan za a zarce da shi sashin masu manyan laifika na bursin din kurmawa” “to Allah ya kiyaye” Halima ta ce, “ameen” Zahra ta amsa mata cikin nutsuwa tare da mayar da hankalinta kan tukin da ta ke lokacin da ta ke karya kwana domin hawa kan titin mission road. Tafiyar minti biyar ce ta kaisu sashen masu manyan laifuka na ofishin ‘yan sandan kasancewar babu nisa a tsakaninsu, Zahra ta samu waje ta yi parking a wajen da aka tanada domin ajje motoci sannan suka fito suna tafiya cikin nutsuwa suka jera domin shiga cikin ofishin ‘yan sandan. 13(ZAHIRIN KAUNA LITTAFI NA DAYA, NA NURA S GARO) Kai tsaye sashen masu kula da manyan laifi suka tunkara kasancewar ba wannan ba ne karon farko da suka fara shiga cikin ofishin kusanma ya zamar musu jiki domin duk wani babban laifi tanan suke fara bincikensa kafun su shiga kotu. Inspector Bashir suka tarar yana zaune a kan kujerarsa ya dunkufar da kai yana rubuce-rubuce, sallarmar da su Zahra suka yi ce ta sa ya dago da kansa da sauri da murmushi a kanfuskarsa ya amsa musu domin sun saba da shi sosai. “lallai yau muna da manyan baki, Barrister Zahra, Barrister Halima sannunku da zuwa” “yauwa sannunka da aiki Bashir” Barrister Zahra ta amsa mishi da murmushi a kan fuskarta lokacin da suke kokarin zama a kan kujerun da ke jere a gaban table din ofishinnasa. Da sauri Inspector Bashir ya mike yana cewa, “bari na kawo muku lemo” “a’a Inspector barshi kawai yanzu muka gama karyawa sannan muka fito mungode” Barrister Halima ce ta dakatar da shi don haka ya koma ya zauna tare da nutsuwa ya basu dukkan hankalinsa. Barrister Zahra ce ta yi gyaran murya lokacin da taga Inspector bashir ya nutsu yana sauraronsu sannan ta fara da cewa, “Bashir daman muna da wani case ne wanda za a shiga kotu gobe, shi ne muka biyo bayan wanda ake zargi domin yi mishi wasu tambayoyi” Inspector Bashir ya daga mata kai cikin girmamawa tare da janyo Computer da ke gabansa yana kallo ya ce, “haka ne Hajiya, ya sunan suspect din na duba muku?” “Alhaji Mukhtar Mai Gaskiya” da sauri Inspector Bashir ya kalli Barrister Zahra da alamun damuwa akan fuskarsa ya ce, “Hajiya anya kuwa kin san Barristan da zaki kara da shi a kotu kuwa?” Barrister Zahra ta kalli Inspector Bashir babu alamun faduwar gaba a kan fuskarta ta ce, “eh Barrister Haidar ko?” “eh shi ne” Inspector Bashir ya bata amsa har a lokacin da alamun damuwar a kan fuskarsa. Barrister Zahra da Halima sukai murmushi cikin nuna karfin gwiwa suka kalli juna sannan suka mayar da kallonsu kan Inspector Bashir, Barrister Zahra ta ce, 14(ZAHIRIN KAUNA LITTAFI NA DAYA, NA NURA S GARO) “na sani, ai shari’a ce Inspector ba da wanda bata hadawa. takan hada Uba da [ansa ko Miji da Matarsa don haka ba laifi ba ne dan Malami da [alibarsa sun goga a wannan karon” Inspector Bashir ya gyada mata kai ya ce, “haka ne Hajiya, nima ba wani abu na gujemiki ba sai record nasan dukkan wani lauya yana takama da irin nasarorin da ya yi a shari’arsa sannan yana kiyayewa domin kare darajarsa” Barrister Zahra ta ce, “haka maganarka ta ke, kamar yadda yanzunma Allah ne kadai ya san mai gaskiya da kuma wanda zai yi nasara” “to Allah ya bada sa’a” Bashir ya ce, sannan ya mayar da hankalinsa wajen shigar da sunan da ya ke a cikin computar bayan ya gama ne ya mike tsaye jikinsa ba kwari ya ce, “muje na kaiku inda ya ke” “to Bashir mungode” Suka ce mishi a tare lokacin da suke mikewa tsaye, Bashir ya shiga gaba suna biye da shi a baya har dakin da aka kulle Alhaji Mukhtar, wanda suka tarar da shi yana zaune ya dunkufar da kai tare da juyawa kofar dakin baya, ya yi shiru baya ko kwakwkwaran motsi. Inspector Bashir ya kallesu ya ce, “to Hajiya ni zan koma sai kun fito” “mun gode” Suka amsa mishi a tare Bashir ya juya ya tafi ya barsu a tsaye a bakin kofar dakin da Alhaji Mukhtar ke kulle inda suka zubawa dattijon mutumin ido suna kallonshi na dan wani lokaci ba tare da sun yi mishi maganaba. Sun kwashe tsawon minti biyu zuwa uku bawanda ya yi magana sannan Barrister Zahra ta yi gyaran murya tare da yi mishi sallama. “assalamu alaika” “ameen wa’alaikumussalam” Tattausar muryar dattijon ta daki dodan kunnensu, wanda ke magana cikin nutsuwa da kamala tamkar ba shi ake zargi da hukuncin kisan kai ba. Barrister Zahra ce ta ci gaba da magana da cewa, “sunana Barrister Zahra Muhammad, wannan kuma abokiyar aikina ce Barrister Halima Mahmoud. Mu ne lauyoyin da zamu kareka a shari’ar da za a gudanar gobe in Allah ya kaimu shi ne muka zo domin mu yi maka wasu tambayoyi da muke fatan zaka bamu hadin kai domin mu gudanar da aikinmu cikin nasara” 15(ZAHIRIN KAUNA LITTAFI NA DAYA, NA NURA S GARO) Barrister Zahra ta kai karshen maganar da ta ke amman tamkar tana fadawa dutse domin dattijon mutumin ko kwakwkwaran motsi bai yi ba tun daga amsa sallamar da ya yi ballantana ya waigo ya kulasu kamar yadda suka bukataba. “danka Umar Mukhtar shi ya daukemu a matsayin lauyoyin da zamu kareka” Ambaton sunan ‘danka Umar Mukhtar’ da Barrister Zahra ta yi ne ya sa a hankali dattijon mutumin ya waigo cikin nutsuwa ya kallesu da tattausan murmushi a kan fuskarsa, suka bishi da kallo a tare. Fari ne, yana da doguwar fuska mai cike da farar kasumba. Kallo daya zaka yi mishi ka fahimci akwai nutsuwa da jin dadi a tattare da shi, ga wani tattausan murmushi bayyane a kan fuskarsa wanda suka kasa gane murmushin me ya ke. ya dauki wasu ‘yan dakiku yana kare musu kallo yayinda murmushin kan fuskarsa ke kara fadada sannan ya taso tsam daga inda ya ke zaune, ya karasa bakin kofar ya dafa karfen da ya yi mishi iyaka da su Barrister Zahra. “barkanku da zuwa” Alhaji Mukhtar ya katse musu tunanin da suke ta hanyar yi musu magana sannan ya zuba musu ido yana kallonsu. “barka dai Baba” Barrister Halima ta yi karfin halin amsa mishi sannan ta sa hannu ta ta6a Barrister Zahra ganin ta kurawa dattijon mutumin ido tana kallonshi cikin mamaki bata ko kiftawa. Ganin Barrister Zahra ta dan nutsu ne ya sa Halima ta mayar da kallonta kan dattijon mutumin cikin tausasa murya domin ba shi girmansa ta fara yi mishi magana da cewa, “Baba wasu tambayoyi muke son yi maka, muna fatan zaka bamu hadin kai ka fadamana gaskiyar abunda ka sani” Alhaji Mukhtar ya fadada murmushin kan fuskarsa ya ce, “insha Allahu ‘yata, zan baku cikakken bayani duk da nasan [ana bai turoku wajena domin ku yi nasara ba, ya turomun ku ne kawai domin ya nunamun soyayya da kulawa” Mamakin Barrister Zahra ya kara munana jin bayanin da ke fita daga cikin bakin Alhaji Mukhtar, lokaci daya duk ta dabarbarce ta kasa yimai tambayar da ta ke son yi mishi. Barrister Halima ce ta kara yin ta maza a karo na biyu ta ce,
No comments:
Post a Comment